Sarkin Tikau na jihar Yobe ya rasu

0
168

Daga Ibraheem El-Tafseer

Da yammacin ranar juma’a ne, Allah ya yiwa mai martaba sarkin Tikau, Alhaji Muhammad Abubakar Grema OON, rasuwa. Mai Tikau ya rasu ne sakamakon doguwar jinya da ya yi fama da ita.

Fadar mai martaba sarkin Tikau tana garin Sabon Garin Nangere da ke ƙaramar hukumar Nangere a jihar Yobe. Ya rasu ne a Asibitin ƙwararru da ke garin Potiskum (Yobe State Specialist Hospital Potiskum).

KU KUMA KARANTA: Ɗan Majalisar Tarayya daga Jigawa ya rasu

Zuwa haɗa wannan rahoto, fadar Mai Tikau ba ta cire sanarwa na lokacin jana’izarsa ba. Amma ana sa ran za a yi jana’izar gobe Asabar a fadarsa da ke Sabon Garin Nangere.

Leave a Reply