No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tankokin yakin Isra’ila sun shiga birnin Rafah da ke kudancin Zirin Gaza, inda suka kai kusan mita 200 daga tsallaken Masar, kamar yadda wani jami’in tsaron Falasɗinu da wani jami’in Masar suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AP.

Jami’in na Masar ya ce da alama “aikin” yana da iyaka. Shi da tashar talabijin ta Al-Aqsa ta Hamas sun ce jami’an Isra’ila sun sanar da Misirawan cewa dakarunsu za su janye bayan kammala aikin.

KU KUMA KARANTA: Turkiyya ce ta aika da kayan agaji  mafi yawa zuwa Gaza da ya kai tan 50,000 — Erdogan

Jami’in na Masar da ke yankin Rafah na ƙasar Masar da kuma jami’in tsaron Falasɗinawa sun yi magana ne da manema labarai.

Tun da farko a ranar Litinin, Majalisar Ministocin Yakin Isra’ila ta yanke shawarar ci gaba da kai farmakin soji a Rafah, bayan da kungiyar Hamas ta sanar da amincewa da shawarar Masar da Qatar na cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...