No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar Kwastam ta Najeriya ta kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi.

Kwanturolan Kwastam na Jihar Kebbi, Iheanacho Ernest Ojike, ya ce hukumar ta damka wa hukumar tsaro ta DSS wadannan nakiyoyi da aka kama.

Kwanturola Iheanacho Ernest Ojike, ya bayyana cewa an kama nakiyoyin ne a cikin wasu kwalaye 40 da kuma buhuna, kuma masu hatsari ne.

KU KUMA KARANTA: DSS ta sako wacce ta soki gwamnatin Kaduna a Facebook

Iheanacho Ojike ya ce an kama wasu mutum biyu da ke da alaka da makaman kuma an gurfanar da su a gaban kuliya, inda alkali ya ba da umarnin tsare su.

A cewarsa, jami’an tsaron hadin gwiwar kwastam, sojoji, ’yan sanda, DSS da kuma hukumar shige da fice ne suka kama mamakan, bayan samun bayanan sirri.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...