No menu items!

Sample Page Title

Date:

Isra’ila ta kashe Falasɗinawa aƙalla 28, cikinsu har da ƙananan yara da dama, a sabbin hare-hare da ta kai wurare daban-daban a yankin Gaza da ta mamaye, kamar yadda ganau suka shaida wa TRT World da kafafen watsa labaran yankin.

Jiragen yaƙin Isra’ila sun kashe mutum takwas a yankin Tuffah bayan sun kai hari kan wata motar ƴan sanda. Kazalika luguden wutar da Isra’ila ta yi a sansanin al-Maghazi da ke yankin Deir al-Balah na Gaza ya yi sanadin mutuwar aƙalla Falasɗinawa 13.

Haka kuma Isra’ila ta kashe Falasɗinawa bakwai a harin da ta kai wa wasu iyalai a sansanin Yabna da ke birnin Rafah. Ta jikkata mutane da dama a harin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...