Connect with us

Labarai

Mun inganta hanyoyin tafiyar da gwamnatinmu – Gwamnan Zamfara

Published

on

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya ƙara jaddada cewa gwamnatinsa ta kawo gagarumar gyara a hanyoyin tafiyar da gwamnati don samar da ci gaba mai inganci a jihar.

A ranar Litinin ɗin nan ne Gwamnan ya bayyana haka a lokacin da ya ke jagorantar zaman Majalisar zartarwar jihar, wanda ya gudana a fadar gwamnati da ke Gusau.

Kamar yadda ya ke ƙunshe cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya kuma bayyana cewa Gwamnan, wanda shi ne shugaban Majalisar zartarwar ya tunatar da sauran mambobin Majalisar irin ƙalubalen da ake fuskanta a sha’anin mulki don tsamo jihar daga halin da ta ke ciki.

KU KUMA KARANTA: Jiragen yaƙin Najeriya sun yi luguden wuta a sansanonin ƴan ta’adda a Zamfara

Sanarwar ta ce, bayan da Gwamnan ya kammala jawabin sa na maraba, sai aka shiga tattauna muhimman batutuwa don tabbatar da su.

Yayin gabatar da jawabi ga mambobin Majalisar, Gwamna Lawal ya jawo hankalin su kan cewa su kasance masu aiki tare, maimakon kowa ya koma yana harkar gaban sa.

“Ganin yadda muke fuskantar 28 ga watan Mayu na 2024, wanda ranar ce za mu cika shekara ɗaya a ofis, wajibi ne mu ƙididdige abubuwan da muka yi, ya muka sauke nauyin da al’ummar jiha suka ɗora mana, kuma me ya kamata mu yi mu inganta gudanar da ayyukan ci gaban ƙasa da more rayuwa, kamar yadda muka yi wa masu kaɗa ƙuri’a alƙawari a yayin yaƙin neman zaɓe.

“Wajibi ne mu bibiyi abin da muka yi don mu san a ina mu ke, wane shiri za mu yi. Mun yi ƙoƙari sosai wajen canja yanayin aikin gwamnati zuwa yadda ya kamata. Mun kasance masu sanya buƙatun jama’a a birbishin komai, mun sanya gabatar da gyara a harkar tafiyar da gwamnati, tare da inganta hanyoyin kasuwanci. Ba abu ne mai sauƙi ba, amma dai muna samun ci gaba ta hanyar da ta dace. Za mu ci gaba da fafatawa ta tanyoyi masu ma’ana waɗanda za su taimaka wajen samar da harkar shugabanci mai kyau, mai ma’ana ga al’ummar da suka zaɓe mu.

“Gwamnati za ta samu nasara ne idan kowannen ku ya yi aiki tare da juna, maimakon a ɗaiɗaiku, waɗanda aikin ku ya bambanta da na juna. Na sha faɗa cewa, wajibi ne ku yi aiki a tare, ku kauce wa kulle kan ku, sai ku kaɗai. Aiki a tare, ita ce kalmar, duk wanda ya saɓa, to ba ya daga cikin mu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like