No menu items!

Sample Page Title

Date:

Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya sanar da kama mutane 9 game da kisan jami’an ‘yan sanda a yankin Ughelli na jihar Delta.

Babban Sufeton ‘yansandan ya bayyana hakan ne yayin taron Hukumar Gudanarwar Rundunar a ranar Alhamis ɗin nan.

Ya ƙara da cewar, waɗanda aka kama ɗin na taimakawa rundunar da bayanan da za su kai ga kama mutanen dake da hannu a kisan.

A ranar 23 ga watan Fabarairun da ya gabata ne, aka hallaka jami’an ‘yansanda 6 a dajin Ohoro, da ke ƙaramar hukumar Ughelli ta Arewa a jihar Delta.

A wani labarin kuma, waɗansu mutanen 6 da ake zargi da hannu a kisan sun tsere.

KU KUMA KARANTA:’Yan fashi sun kai hari bankuna da ofishin ’yan sanda a Kogi

Kisan na zuwa ne a daidai lokacin da aka hallaka hafsoshin soja 17 a jihar ta Delta mai arziƙin man fetur.

An hallaka sojojin ne a yayin da suke aikin wanzar da zaman lafiya a ƙauyen okuama dake ƙaramar hukumar Ughelli ta Kudu a wani al’amari da ya janyo allawadai a faɗin Najeriya.

A yayin jana’izar sojojin da ya gudana a makon da ya gabata, hukumomin sojin Najeriya sun sha alwashin farauto waɗanda suka kitsa harin, tare da jaddada cewar hakan ba zai hana su cimma burinsu na fatattakar ɓata-gari daga faɗin Najeriya ba.

Haka shima, Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya miƙa lambobin girmamawar ƙasa ga sojojin da hallaka tare da ɗaukar nauyin karatun ‘ya’yansu.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...