No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hotunan tauraron ɗan’adam da cibiyar tauraron ɗan’adam ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi nazari sun nuna cewa kashi 35 cikin 100 na gine-ginen Gaza sun lalace sakamakon hare-haren da Isra’ila ke kaiwa yankin Falasɗinawa.

Hare-haren da Isra’ila ta ƙaddamar a matsayin mayar da martani ga hare-haren Hamas a ranar 7 ga watan Oktoba, ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa kusan 32,000, a cewar hukumomin lafiya a Gaza.

A cikin tantancewar da ta yi, Cibiyar Tauraron Dan’Adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya, UNOSAT, ta yi amfani da hotuna na tauraron ɗan’adam da aka tattara a ranar 29 ga watan Fabrairu tare da kwatanta su da hotunan da aka dauka kafin da bayan fara sabon rikici.

KU KUMA KARANTA: Taron ƙungiyar AU na nemo hanyar warware matsalolin da ke addabar nahiyar Afirka

An gano cewa kashi 35 cikin 100 na dukkan gine-gine a Gaza — gine-gine 88,868 – sun rushe ko kuma sun lalace.

Daga cikin waɗannan, ta gano gine-gine 31,198 da aka lalata, 16,908 sun rushe baki ɗaya, sannan 40,762 sun lalace sosai.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...