Connect with us

Ƙasashen Waje

Blinken zai je Saudiyya da Masar domin tattaunawa kan tsagaita wuta a Gaza

Published

on

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Anthony Blinken zai je Saudiyya da Masar a wannan makon domin tattaunawa kan yadda za a tsagaita wuta a rikicin da ake yi tsakanin Isra’ila da Gaza, da kuma yadda za a ƙara yawan kayan agajin da ake kaiwa Falasɗinu.

KU KUMA KARANTA: Sarkin Saudiyya ya yi ƙira kan kawo ƙarshen munanan laifukan da ake yi a Gaza

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Mattew Miller ne ya bayyana haka inda ya ce Blinken ɗin zai tattauna da jagororin Saudiyya a Jeddah a ranar Laraba inda a ranar Alhamis zai wuce birnin Alkahira na Masar domin tattaunawa da shugabannin Masar.

Isra’ila na ci gaba da kai hare-hare a Gaza a kullum inda take kashe ɗumbin jama’a akasarinsu yara da mata.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Jami’ai a Gaza sun zaƙulo gawawwakin Falasɗinawa 21 daga cikin ɓaraguzai

Published

on

Jami'ai a Gaza sun zaƙulo gawawwakin Falasɗinawa 21 daga cikin ɓaraguzai

Jami’ai a Gaza sun zaƙulo gawawwakin Falasɗinawa 21 daga cikin ɓaraguzai

Jami’an kare farar hula a Gaza sun zaƙulo gawawwaki 21 na Falasɗinawa daga cikin ɓaraguzai a ranar Lahadi bayan wani hari da Isra’ila ta kai a Zirin Gaza.

Wata majiya daga ɓangaren kiwon lafiya ta bayyana cewa an gano gawar mutum shida sakamakon harin da Isra’ila ta kai a birnin Rafah inda aka kai su asibitin Khan Younis.

Haka kuma an ƙara zaƙulo wasu gawawwakin uku daga cikin ɓaraguzai a yammacin Gaza, kamar yadda Hukumar Kare Fararen Hula ta Gaza ta bayyana a wata sanarwa.

READ ALSO: Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 29 a harin da ta kai a wata makaranta a Gaza

Jami’an sun ƙara gano wasu gawawwakin goma a unguwar Tel al-Hawa da ke kudu maso yammacin Gaza.

Sai kuma mazauna sansanin gudun hijira na Nuseirat sun gano gawawwakin mutum biyu a tsakiyar Zirin Gaza, kamar yadda shaidu suka bayyana.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Faɗa da ruwan bama-bamai a birnin Gaza bayan ba da umarnin kwashe jama’a

Published

on

Faɗa da ruwan bama-bamai a birnin Gaza bayan ba da umarnin kwashe jama'a

Faɗa da ruwan bama-bamai a birnin Gaza bayan ba da umarnin kwashe jama’a

An gwabza ƙazamin faɗa da ruwan bama-bamai a birnin Gaza da wasu yankunan Falasɗinawa a yau Juma’a yayin da masu shiga tsakani ke ci gaba da kokarin dakatar da yakin da ya shiga cikin wata na goma.

Shugaban Amurka Joe Biden ya faɗa a taron Ƙungiyar Tsaro ta NATO a birnin Washington jiya Alhamis cewa jami’an diflomasiyyar Amurka, duk da matsalolin da ake fuskanta, suna samun “ci gaba” tare da masu shiga tsakani na ƙasa da ƙasa wajen cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tare da jaddada cewa “lokaci ya yi da za a kawo ƙarshen wannan yaƙi”.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 29 a harin da ta kai a wata makaranta a Gaza

Kafofin yaɗa labarai masu alaƙa da mahukuntan yankin Hamas, sun ce sojojin Isra’ila sun ƙaddamar da sabbin hare-haren sama fiye da 70.

Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta ba da rahoton mutuwar mutum 32, tana mai cewa “an kai waɗanda suka mutun, waɗanda akasarinsu yara da mata ne zuwa asibitoci cikin dare, saboda kisan kiyashin da ake ci gaba da yi”.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce tana kuma gwabza faɗa a yankin Rafah da ke kudancin ƙasar, inda dakarunta suka “kawar da ‘yan ta’adda da dama a hare-hare ta sama”.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Fursunoni sun tsere daga gidan yarin Nijar da ke tsare da masu ta da ƙayar baya

Published

on

Fursunoni sun tsere daga gidan yarin Nijar da ke tsare da masu ta da ƙayar baya

Fursunoni sun tsere daga gidan yarin Nijar da ke tsare da masu ta da ƙayar baya

Ma’aikatar Harkokin Cikin gida ta Jamhuriyar Nijar ta ce ta umarci sassan bincike na ƙasar da su kasance cikin shirin ko ta kwana bayan da fursunoni suka tsere a ranar Alhamis daga gidan yari mai cike da mai tsaro na Koutoukale inda ake tsare fursunonin da suka haɗa da masu ikirarin jihadi.

Sanarwar da ma’aikatar ta fitar ba ta bayyana adadin fursunonin da suka tsere daga Koutoukale da ke da tazarar kilomita 50 daga arewa maso yammacin Yamai babban birnin kasar ba, ko kuma yadda suka yi hakan. A cikin shekarun 2016 da 2019, an taɓa daƙile yunƙurin fasa gidan yarin.

Fursunonin gidan yarin sun haɗa da waɗanda ake tsare da su daga rikicin kasar da kungiyoyin da ke ɗauke da makamai masu alaƙa da al Qaeda da IS da kuma waɗanda ake zargin mayaƙan Boko Haram ne.

Hukumomin yankin sun kafa dokar hana fita da dare a cikin garin Tillaberi, wanda ke yanki ɗaya da gidan yarin, amma ba su yi ƙarin bayani ba.

KU KUMA KARANTA: Fursunoni 118 sun tsere daga gidan yarin Suleja

Jamhuriyar Nijar da maƙwabtanta da ke tsakiyar yankin Sahel na cikin sahun gaba wajen yaƙi da masu ikirarin jihadi da ke ci gaba da ƙaruwa tun shekarar 2012, lokacin da mayaƙan da ke da alaƙa da al-Qaida suka fara ƙwace wasu sassan kasar ta Mali.

Dubban mutane ne aka kashe a cikin tashe-tashen hankulan tare da raba wasu sama da miliyan uku da muhallansu, lamarin da ya ƙara rura wutar rikicin jinƙai a wasu ƙasashe mafiya talauci a duniya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like