No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Anthony Blinken zai je Saudiyya da Masar a wannan makon domin tattaunawa kan yadda za a tsagaita wuta a rikicin da ake yi tsakanin Isra’ila da Gaza, da kuma yadda za a ƙara yawan kayan agajin da ake kaiwa Falasɗinu.

KU KUMA KARANTA: Sarkin Saudiyya ya yi ƙira kan kawo ƙarshen munanan laifukan da ake yi a Gaza

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Mattew Miller ne ya bayyana haka inda ya ce Blinken ɗin zai tattauna da jagororin Saudiyya a Jeddah a ranar Laraba inda a ranar Alhamis zai wuce birnin Alkahira na Masar domin tattaunawa da shugabannin Masar.

Isra’ila na ci gaba da kai hare-hare a Gaza a kullum inda take kashe ɗumbin jama’a akasarinsu yara da mata.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...