Connect with us

Labarai

A yi gaggawar gudanar da bincike kan zargin da Sanata Ningi ya yi – Atiku

Published

on

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ne ya yi wannan kiran a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook inda ya ce yin rufa-rufa kan lamarin da kuma dakatar da wanda ya kwarmata zancen ba mafita ba ce.

Ɗan takarar shugaban ƙasa ƙarƙashin jam’iyyar adawa ta PDP a zaɓen 2023, Atiku, ya ce akwai buƙatar a gudanar da ƙwaƙƙwaran bincike kan zargin cushe a kasafin kuɗin Najeriya na 2024.

A ‘yan kwanakin nan ne Sanata Abdul Ningi da ke wakiltar mazaɓar tsakiyar yankin jihar Bauchi a Majalisar Dattawa, ya yi zargin cewa an yi cushen sama da Naira tiriliyan uku a kasafin kuɗin 2024.

Majalisar ta musanta zargin ta kuma dakatar da shi tsawon watanni uku daga halartar zaman majalisar bayan da akasarin mambobinta suka amince da hakan.

Sai dai Atiku ya ce ‘yan Najeriya na da haƙƙin su ga an gudanar da bincike kan zargin da Ningi ya yi.

“Musanta cewa babu wani abu kamar haka, da dakatar da Sanatan da ya kwarmata zancen, ba za su hana zargin cewa akwai matsalar cin hanci da rashawa da kashe kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba da gwamnatin tarayya ke yi.

“Ba zai yi wu a yi rufa-rufa kan zargin yin cushe a kasafin kuɗi da yawansa ya kai Naira tiriliyan uku ba.” In ji Atiku.

KU KUMA KARANTA:Manyan Sanatoci sun kai wa Tinubu ziyara bayan dakatar da Sanata Ningi

Atiku ya ƙara da cewa, “duba da irin wahalar da ake fuskanta a Najeriya, cushe a kasafin kuɗin ƙasa na nufin karin yunwa, talauci, rashin tsaro da rashin wutar lantarki da matsalar canja kudaden ƙasashen waje da kuma tsadar rayuwa.”

“Babu yadda za a ce ‘yan Najeriya za su naɗe hannayensu suna kallo a yi watsi da wannan zargi da ke kara ta’azzara matsalar tattalin arziƙinmu.” In ji Atiku.

Najeriya ta ware Naira tiriliyan 28.7 a matsayin kasafin kuɗin shekarar 2024.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like