No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sarki Salman na Saudiyya ya yi ƙira a cikin saƙonsa na watan Ramadan ga ƙasashen duniya da su kawo ƙarshen munanan laifukan da ke faruwa a Gaza, inda Isra’ila ta shafe sama da watanni biyar tana gwabza yaƙi a yankin.

Da yake magana a matsayin mai kula da wurare biyu mafi tsarki na Musulunci, Sarki Salman ya yi godiya kan “yadda aka albarkaci Masarautar Saudiyya”, amma ya ce yaƙin da ake yi a Gaza da aka yi wa ƙawanya zai sa a yi azumi da sauran ibadu cikin rashin walwala.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe gomman Falasɗinawa a ranar farko ta Azumin Ramadana

“Yayin da muke maraba da shigowar watan Ramadan a wannan shekara,ranmu ya yi matuƙar ɓacin kan yadda ‘yan’uwanmu Falasɗinawa ke ci gaba da fuskantar hare-haren wuce-gona-da-iri,” in ji shi.

“Muna ƙira ga ƙasashen duniya da su kiyaye nauyin da ke wuyansu na kawo ƙarshen waɗannan munanan laifuka tare da tabbatar da kafa hanyoyin jinƙai da na agaji.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...