Connect with us

Labarai

’Yan sa kai sun yi wa limami yankan rago a Zamfara

Published

on

Jami’an tsaron sa kai na gwamnatin Jihar Zamfara (CPG) sun yi wa Babban Limamin Masallacin Juma’a na garin Mada, Imam Abubakar Hassan, yankan rago.

Wata majiya mai kusanci da marigayin ta ce jami’an sa kai biyar ne suka zo kauyen da ke Ƙaramar Hukumar Gusau a kan babura suka ɗauki marigayin bayan sallar La’asar ranar Lahadi.

“Lokacin da suka kama shi, mun yi tunanin ana gayyatar sa ne kan wata magana ko don gudanar da bincike, amma sai muka tsinci gawarsa a jefe a bayan gari.

“’Yan bangan sun yi wa limamin yankan rago ne. Ta yaya za a yi wa mutum irin wannan kisa?

“Marigayi shugaba ne mai natsuwa, kuma mai saukin kai, ba mu taba sanin sa da wani mummunan hali da zai sa a kashe shi ba.”

KU KUMA KARANTA: MƊD ta tabbatar da sace mata ’yan gudun hijira sama da 200 a Borno

Wani mazaunin garin, Muhammad Yunus ya bayyana kisan babban limamin a matsayin wani abu mai kama da siyasa ko bita da kulli.

Ya ce, Malam ya taba tsaya wa wadansu matasa biyu da ’yan banga suka kama bisa zargin su da hannu a fashi, bara.

“Na yi imanin wannan abin ne ya sa ’yan bangar, suka kashe Imam.

Babban kwamandan ’yan Sa Kai na Jihar Zamfara, Kanar Rabi’u Yandoto ya tabbatar da faruwar lamarin.

A cewara, kawo yanzu abin da aka iya ganowa shi ne ’yan sa kai na zargin sa da taimakawa masu garkuwa da mutane da satar shanu.

Kanar Yandoto ya bayyana cewa, hedikwatar CPG ba ta san komai game da kamun da aka yi wa babban limamin, inda ya kara da cewa “a ka’ida, idan muna zargin mutum muna kamo shi ne domin bincike, ba kashewa ba.

Don haka, wannan kisa ba bisa ka’ida aka yi ta ba, an aikata haramun kuma za a yi bincike.

“Ba mu ba jami’anmu umarnin kama kowa ba, don a yanzu haka jami’an CPG biyu da ake zargi da kisan babban limamin suna hannun mu; daga Mada aka kawo su kuma za mu yi musu tambayoyi bisa zargin da ake musu.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like