No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ma’aikatar Lafiya ta Falasɗinu ta ce adadin Falasɗinawan da suka mutu sakamakon yunwa a Gaza ya ƙaru zuwa 18 sakamakon takunkuman da Isra’ila ta ƙaƙaba musu.

A cikin wata sanarwa da kakakin ma’aikatar Ashraf al Qudra ya fitar, ya ce “yunwa a arewacin Gaza ta kai matakin illata mutane, musamman ga yara da mata masu juna biyu da masu fama da cututtuka masu tsanani.

Ya yi gargaɗin cewa dubban mutane na cikin haɗarin mutuwa saboda yunwa, inda ya yi ƙira da a gaggauta kai agajin jinƙai da jinya ga yankin Falasɗinu.

KU KUMA KARANTA: Matakan da gwamnatin Najeriya ta ɗauka na ƙayyade farashi ba zai kawar da yunwa ba – Masana

Kakakin ya zargi sojojin Isra’ila da “da aikata mummunan kisan kiyashi da gangan akan dubban mutanen da ke fama da yunwa a arewacin Gaza.”

Ya yi ƙira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da ta dauki matakan gaggawa “don hana afkuwar bala’in jinƙai da lafiya a arewacin Gaza.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...