An kama mutane da dama a sabon farmakin da Isra’ila ta kai a Yammacin Gabar Kogin Jordan da ta mamaye

Sojojin Isra’ila sun kama wasu Falasɗinawa 55 a farmakin da sojojin suka kai a Yammacin Gaɓar Kogin Jordan da suka mamaye, a cewar ƙungiyoyin da ke kula da fursunoni.

A cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da hukumar kula da fursunonin Falasɗinawa ta fitar ta ce, an kai aƙalla mutum 22 hannun Isra’ila a birnin Hebron, yayin da wasu kuma aka kama su a garuruwan Bethlehem da Ramallah, da ke Gabashin Kudus da kuma Qalqilya.

KU KUMA KARANTA: Ya kamata Falasdinawa su yi fito na fito da Isra’ila a lokacin azumin Ramadan — Hamas

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Kamen na nuni da ayyukan zagon ƙasa da lalata gidajen ‘yan kasar, baya ga mummunan duka da ake yi wa fursunonin da iyalansu, da kuma ƙwace kuɗaɗe.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *