No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hamas na ƙira ga Falasɗinawa a Isra’ila da Gabar Yammacin Kogin Jordan da aka mamaye da su tashi tsaye don nuna adawa da mamayar Isra’ila a cikin watan Ramadan mai alfarma da ke gabatowa.

Mai magana da yawun ƙungiyar Hamas, Osama Hamdan, da yake zantawa da manema labarai a birnin Beirut, ya ce Falasɗinawa su sanya kowane lokaci na watan Azumin ya zamo wata arangama.

KU KUMA KARANTA: Hana Falasɗinawa shiga Masallacin Ƙudus a watan Ramadan na iya haifar da tashin hankali – ‘Yan sandan Isra’ila

Ƙasashen Amurka da Qatar da Masar dai sun kwashe makonni suna ƙoƙarin ganin an tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas a Gaza da kuma shawo kan ƙungiyar masu fafutukar ganin an sako wasu adadi mai yawa na mutanen da ake garkuwa da su a harin na ranar 7 ga watan Oktoba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...