Connect with us

Labarai

Tinubu ya umarci Ɗangote da BUA su rage farashin siminti

Published

on

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umarci kamfanin Ɗangote da BUA da su rage kudin farashin buhun siminti don samar wa al’umma sauki daga matsin rayuwa da ake fuskanta.

Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi ne, ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ziyara da ya kai masana’antar siminti ta BUA da ke Sakkwato a ranar Alhamis.

Babban Darakta a kamfanin BUA, Alhaji Kabiru, ya ce a halin yanzu suna sayar da buhun siminti kan kuɗi naira 6000, don cika alkawarin da suka yi daukar wa shugaban kasa cewa ba za su sayar da buhun siminti sama da 7000 ba.

“Game da batun farashin siminti, zan iya cewa har yanzu suna yin abin da ya dace kamar yadda suka tattauna da shugaban ƙasa.

KU KUMA KARANTA: Kamfanonin siminti za su rage farashinsa a Najeriya

“Shugaban ƙasa ya jaddada batun dawo da farashin baya domin sauƙaƙa wa talaka.

“Ina so na ƙara musu ƙwarin gwiwa don su bi umarnin shugaban ƙasa domin mu cimma shirin samar da gidaje da kuma sabbin hanyoyin gina rayuwa kamar yadda shugaban kasa ya bukata,” in ji shi.

A baya-bayan nan dai kayayyaki sun yi tashin gwauron zabi a Najeriya, lamarin da ya sanya talakawa kokawa.

Farashin kuɗin buhun siminti ya ninka kudinsa na baya, inda a wasu jihohi ake sayar da shi daga Naira 10,000 zuwa 15,000.

A makon da ya gabata, Shugaba Tinubu ya gana da shugabannin kamfanonin siminti da ke kasar nan, don tattauna yadda za a daidaita farashin simintin.

A gefe guda kuwa, ƙungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC sun gudanar da zanga-zangar kwanaki biyu a ranar Talata da Laraba, don neman gwamnatin tarayya yi wani abu kan tsadar rayuwa a Najeriya.

Shugaba Tinubu dai ya roki ‘yan Najeriya da su kara hakuri kan yanayin da ake ciki, wanda a cewarsa yana aiki tukuru don samar wa da talaka sauƙi daga halin da ake ciki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like