No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Wata Ƙungiyar arewa da ke sanya idanu kan harkokin tattalin arziƙi (Arewa Economic Forum), ta yi tsokaci kan halin da tattlin arziƙin ƙasar ke ciki, inda ta yi ƙira ga shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya sake nazari kan manufar cire tallafin man fetur da kuma dakatar da raba kuɗaɗen da ake yi wa gwamnonin jihohi.

Shugaban ƙungiyar, Alhaji Shehu Ibrahim Ɗandakata, wanda ya yi jawabi ga manema labarai a ranar Alhamis a Abuja, ya ce rashin bin diddigi da kuma rashin mai da hankali kan muhimman abubuwa da gwamnoni ke yi shi ya sa talauci da yunwa suka yi ƙamari a ƙasar.

A madadin sake dawo da biyan tallafin man fetur, ƙungiyar ta yi ƙira ga shugaban ƙasa da ya nemo hanyoyn da za a tabbatar da cewa gwamnonin jihohi sun yi amfani da rarar kuɗaɗen da ake kasafta musu ta hanyoyin da suka dace domin kuɗaɗen su yi tasiri kan al’umma.

KU KUMA KARANTA: DSS ta gargaɗi ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya a kan shirin zanga-zangar ‘tsadar rayuwa’

Ɗandakata ya kuma buƙaci gwamnatin tarayya da ta duba halin da darajar kuɗin ƙasar ke ciki, ta kuma binciki dalilin da ya sa farashin dala ke tashi bayan duk wani taron kwamitin raba arziƙin ƙasa (FAAC).

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...