Connect with us

Labarai

Nahiyar Afirka na fuskantar barazana daga ƙungiyar IS – MƊD

Published

on

Nahiyar Afirka har yanzu na ci gaba da fuskantar barazana daga ƙungiyar masu tsattsauran ra’ayin addini ta IS yayin da ake fama da tashe-tashen hankula na siyasa a yammacin Afirka da yankin Sahel.
Ƙungiyar kuma har yanzu tana da niyyar kai hare-hare a ƙasashen waje, in ji jami’in yaƙi da ta’addanci na Majalisar Ɗinkin Duniya (MƊD) a ranar Alhamis.

Vladimir Voronkov ya sake nanata binciken da Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi na cewa ƙungiyar IS na ci gaba da yin barazana ga zaman lafiya da tsaro a duniya, musamman a yankunan da ake fama da rikici, duk kuwa da gagarumin ci gaba da ƙasashe mambobin MƊD suka samu wajen tunkarar wannan barazana. Voronkov ya ce ƙungiyar ta kuma ƙara kai hare-hare a tsoffin tungar ta Iraƙi da Siriya da kuma kudu maso gabashin Asiya.

Voronkov ya shaidawa kwamitin sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya cewa, lamarin ya taɓarɓare a yammacin Afirka da Sahel, “kuma yana ƙara sarƙaƙewa,” yayin da rikicin ƙabilanci da na yanki ya shiga cikin ajanda da ayyukan ƙungiyar masu tsattsauran ra’ayi. , wanda kuma aka fi sani da sunansa na Larabci, Daesh, da masu alaka da shi.

Ya ƙara da cewa, masu alaƙa da ‘yan ta’addar Daesh suna ci gaba da gudanar da ayyukansu tare da samun ‘yancin cin gashin kansu daga cikin ƙungiyar ta Daesh, yana mai gargaɗin cewa idan har aka ci gaba da yin hakan akwai hatsari “babban yanki na iya fuskantan rashin zaman lafiya daga ƙasar Mali zuwa kan iyakokin.

KU KUMA KARANTA:Ƙungiyar ƙwadago za ta yi zanga-zanga saboda tsadar rayuwa

Natalia Gherman, babban darektan kwamitin zartarwa na kwamitin yaƙi da ta’addanci na Majalisar Ɗinkin Duniya, ta ce: “Suna amfani da rashin zaman lafiya don faɗaɗa tasirinsu, da ayyukansu akan yankunan Sahel, tare da ƙara nuna damuwa ga gaɓar tekun yammacin Afirka.”

“Nahiyar Afirka yanzu ta kai kusan rabin adadin ayyukan ta’addanci na duniya, inda tsakiyar Sahel ke da kashi 25% na irin waɗannan hare-hare,” kamar yadda ta shaida wa majalisar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like