Connect with us

Labarai

Farashin kayayyakin masarufi na ci gaba da tashi a Najeriya

Published

on

Farashin kaya a Najeriya na ci gaba da tashi babu ƙaƙƙautawa a farkon shekara nan, kamar yadda hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS ta bayyana a rahoton da ta fitar.

Hukumar ta ce farashin kayayyaki ya yi matuƙar tashi a watan Junairun shekarar nan, inda farashin ya ƙaru da kaso 8.8 cikin ɗari, idan aka kwatanta da yadda farashin yake a watan Janairun shekarar 2023.

Rahoton ya ce farashin kayayyaki sun ci gaba da hauhauwa a farkon shekarar da aka shiga, fiye da yadda farashin yake a watan Disambar shekarar da ta gabata.

Hukumar NBS ta ce, farashin kayayyakin abinci a Najeriya ya yi matuƙar tashi a watan Janairun da ta gabata, inda farashin ya ƙaru kuma ya kai kaso 35.41 cikin ɗari bisa ma’auni, wanda hakan ya nuna cewa farashin ya ƙaru da kaso 11.10 cikin ɗari, idan aka kwatanta da yadda yake a watan Janairun shekarar 2023, inda farashin yake a matsayin kaso 24.32 cikin ɗari.

Farashin kayayyakin masarufi da sauran nau’ukan kayayyaki sun ci gaba da hauhauwa a ƙasar biyo bayan cire tallafin man-fetur da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi lokacin kama rantsuwar aiki.

Hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya ya zamo wani abu da ‘yan ƙasar ke ta kokawa akai, wanda kuma hakan ya sa wasu ke rayuwa da abin kalace sau ɗaya a yini.

KU KUMA KARANTA:Masu Biredi a Najeriya na shirin tsunduma yajin aiki saboda tsadar kayan hada Biredi

A hirarsa da Muryar Amurka, Nasiru Shu’aibu Marmara masani kuma manazarci kan lamuran da suka shafi tattalin arziƙi da ci gaban ƙasa, ya ce “yadda farashin kayayyaki yake tashi a Najeriya, babban barazana ne ga tattalin arziƙin ƙasar, duk da cewa anyi hasashen faruwar hakan, idan aka duba yadda aka ɗaura tubalin tafiyar da tattalin arziƙin ƙasar.”

Nasiru Shu’aibu ya ƙara da cewa “Gwamnati yanzu tana ƙoƙarin ganin ta ƙara samar da hanyar kuɗin shiga ga ‘yan ƙasar, domin ya zo daidai da yadda farashin kaya yake a ƙasar.”

Yanzu dai hankulan yan ƙasar ya karkata ne ga mahukunta, domin ganin yadda za su shawo kan lamarin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like