No menu items!

Sample Page Title

Date:

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa abinci zai ƙara ƙaranci a watanni masu zuwa a daidai lokacin da Sudan ke shiga watannin ƙarancin abinci.

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya FAO ta yi gargaɗi a Geneva cewa irin ɓarnar da farin ɗango suka yi wa amfanin gona ya yi matuƙar haddasa matsaloli tun daga tsakiyar shekarar da ta gabata.

Mataimakin wakilin FAO a Sudan Adam Yao ya yi gargaɗi kan cewa matsalolin farin ɗangon sun kai wani “mataki na barazana”, kuma ba tare da tsare-tsare masu ɗorewa ba na daƙile bazuwarsu ba, za a ci gaba da tafka asara.

Wannan na faruwa ne sakamakon rashin ayyukan sa ido a tsakiya da yammacin Sudan sakamakon yaƙin da ake gwabzawa tsakanin sojojin ƙasar da kuma dakarun RSF.

KU KUMA KARANTA: Tallafin abinci na ‘yan gudun hijirar Sudan a Chadi yana dab da ƙarewa – MƊD

A wani ɓangaren, jami’an da ke sa ido kan farin ɗango tare da goyon bayan FAO sun yi ƙoƙarin sa ido kan sama da kadada 113,500 da kuma aiki a kan kadada 23,000 wadda farin suka yi wa ɓarna.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce ana ƙiyasin cewa mutum miliyan 18 suna fama da ƙarancin abinci – wanda hakan ke nufin an samu ƙarin mutum miliyan goma fiye da bara.

Hukumomin bayar da agaji sun yi ƙoƙarin kai kayan agaji ga mutum miliyan bakwai a Sudan tun daga Afrilun bara.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...