No menu items!

Sample Page Title

Date:

Saudiyya ta shaida wa Amurka matsayinta na cewa ba za ta ƙulla hulɗar diflomasiyya da Isra’ila ba, matuƙar ba a amince da ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kanta a kan dokokin 1967 ba, da kuma sanya Gabashin Birnin Kudus, a matsayin babban birninta, kuma har sai Isra’ila ta dakatar da kai wa kan Gaza da aka yi wa ƙawanya hare-hare, in ji Ma’aikatar Harkokin Wajen Saudiyya a wata sanarwar.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 30 da ke tsare a hannunta a Gaza — Ƙungiyar Fursunonin Falasɗinu

A ranar Talata, mai magana da yawun Fadar White House John Kirby ya ce gwamnatin Biden ta sami martani mai kyau cewa Saudiyya da Isra’ila a shirye suke su ci gaba da tattaunawar daidaitawa.

Ma’aikatar ta ce Masarautar ta fitar da sanarwar ne domin tabbatar da tsayuwarta tsayin daka ga Washington kan batun Falasɗinu bisa la’akari da kalaman da ake dangantawa da Kirby.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...