Connect with us

Ƙasashen Waje

Zanga-zanga ta ɓarke a Senegal bayan sanar da ɗage zaɓe

Published

on

Jami’an tsaron Senegal sun tarwatsa dandazon jama’a da suka taru a Dakar babban birnin ƙasar ranar Lahadi domin nuna adawa da ɗage zaɓen shugaban ƙasar da aka yi, wanda a da za a yi shi ne a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Shugaba Macky Sall ya sanar a ranar Asabar da ta gabata cewa za a jinkirta kaɗa ƙuri’ar zuwa ranar da ba a bayyana ba saboda taƙaddama kan jerin sunayen ƴan takara – matakin da jam’iyyun adawa suka yi watsi da shi.

Kimanin masu zanga-zanga 200 ne suka hana zirga-zirgar ababen hawa a babban titin birnin Dakar tare da saka shingayen na ƙonannun tayoyi, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

An kama tsohuwar Firaiministar Senegal Aminata Toure, wadda a yanzu ita ce babbar ‘yar gaba-gaba a zanga-zangar nuna adawa da ɗage zaɓen shugaban ƙasa, kamar yadda ɗan majalisar jam’iyyar adawa Guy Marius Sagna ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP.

“Na tabbatar da cewa ‘yan Jandarma sun kama Aminata Toure,” in ji shi. Shugaban ƙasar Macky Sall ne ya naɗa Toure firaiminista amma daga baya ta koma jam’iyyar adawa.

Ƴan zanga-zangar

Ɗaruruwan magoya baya na adawa da ke zanga-zangar sun koma kan gefen titunan bayan ‘yan sandan kwantar da tarzoma sun harba hayaƙi mai sa hawaye. Har yanzu dai hukumomin ƙasar ba su ce komai ba kan sabon lamarin.

KU KUMA KARANTA: ECOWAS ta damu kan ɗaga zaɓen shugaban ƙasa a Senegal

Senegal dai ba ta taɓa jinkirta zaɓen shugaban ƙasa ba kuma akwai rashin tabbas kan abin da zai biyo baya.

A bara, ƙasar ta fuskanci mummunar zanga-zanga bayan da aka ɗaure jagoran ƴan adawa Ousmane Sonko, inda magoya bayansa suka ce wata dabara ce ta hana shi tsayawa takara a zaɓen.

Shekaru da dama ana kallon Senegal a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen Yammacin Afirka mafi kwanciyar hankali a tsarin dimokuraɗiyya, amma rashin ci-gaban siyasa a ƙasar ya haifar da damuwa.

Bayan sanarwar da Sall ya yi ta kafar talabijin, ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Yammacin Afirka ta ECOWAS ta nuna damuwa game da yanayin da ya kai ga ɗage zaben, tare da yin kira da a sanya sabuwar ranar zaɓe cikin gaggawa. An kuma buƙaci a kwantar da hankula da bin matakin sasantawa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like