No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa an kai hari a Hedkwatarta da ke Maiduguri babban birnin jihar Borno.

Ta bayyana haka ne a wata sanarwa da mai magana da yawunta na jihar ta Borno ASP Nahum Daso Kenneth ya fitar ranar Asabar da maraice.

Kenneth ya ce ba a kai hari a “Hedkwatar rundunar ‘yan sanda ta jiha da ke Maiduguri ba” kuma tana karkashin kulawar jami’an tsaro sannan tana aiki.

Sai dai ya ƙara da cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari a Unguwar ‘Yan sanda da ke “garin Gajiram na ƙaramar hukumar Nganzai” ranar 2 ga watan Fabrairu da tsakar dare lamarin da ya yi sanadin mutuwar wasu dakarunsu.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Bauchi sun bankaɗo bindigogin AK-47 da miliyan 4.5 a maɓoyar masu garkuwa da mutane

“Kwamishinan ‘yan sanda CP MI Yusufu ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan ‘yan sanda huɗu da suka rasa rayukansu a yayin da suke kare unguwar ‘yan sanda ta Gajiram a Nganzai,” in ji sanarwar.

Borno na ci gaba da fuskantar hare-hare daga mayakan Boko Haram da na ISWAP waɗanda suka kwashe shekaru da dama suna addabar jihar.

Mayakan sun kashe dubban mutane tare da raba miliyoyi da gidajensu, baya ga sace mutane ciki har da ɗalibai.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...