Ƙasashen Waje
Amurka ta kai harin ramuwar gayya a Syria da Iraki
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/02/Screenshot_20240203-111646_1.jpg)
Rundunar sojin Amurka ta ce dakarunta sun ƙaddamar da jerin hare-hare ta sama a wasu yankuna na Syria da Iraki domin yin ramuwar gayya kan kisan sojojinsu uku da aka yi a wani sansanin sojin Amurka da ke kan iyakar Jordan da Syria.
Dakarun sojojin Amurka sun kai hare-hare kan runduna ta musamman ta Revolutionary Guards ta Ira da kuma ƙungiyoyin masu tayar da kayar baya da ke da Tehran inda hare-haren suka sauka a fiye da yankuna 85 a Iraki da Syria, a cewar rundunar ranar Juma’a.
“An kai hare-haren na sama ne da makamai fiye da 125 da ke iya sauka a wurin da aka cilla su ba tare da kuskure ba,” a cewar Rundunar da ke bayar da umarni ta sojojin Amurka a wani sako da ta wallafa a soshiyal midiya.
KU KUMA KARANTA: Amurka ta sake nanata ƙudurinta na tsayawa tsayin daka a fannin tattalin arziƙi da kasuwanci a ƙasashen Afirka.
Ta ƙara da cewa an kai hare-haren ne a cibiyoyin bayar da umarnin soji da na leƙen asiri da rokoki da makamai masu linzami da wuraren ajiye jirage marasa matuka na masu tayar da kayar baya da kuma dakarun tsaron Iran “waɗanda suke taimaka wa wurin kai hare-hare kan Amurka da kawayenta.”
Shugaba Joe Biden ya jaddada cewa Amurka za ta ƙara ƙaimi wurin mayar da martani. “Mun soma mayar da martani yau kuma za mu ƙara ƙaimi wurin yin hakan a wurare da lokutan da muka sanya wa ido,” in ji Biden.
“Duk da yake Amurka ba ta tsokanar faɗa a Gabas ta Tsakia da wasu yankuna, ina so na bayyana ƙarara cewa duk wanda ya ce mana kule, za mu masa cas,” a cewar shugaban Amurka.
Jami’an gwamnatin Iraki sun yi tir da waɗannan hare-hare a kan iyakokinsu, suna masu cewa hakan ya ƙeta alfarmarsu ta kasancewa kasa mai cin gashin kanta sannan za su nuna fushinsu mai girma.
Janar Yehia Rasool, kakakin Firaiminista Mohamed Shia al Sudani, ya yi gargadi cewa harin da aka kai a yammacin Iraki, kusa da kan iyaka da Syria, zai iya jefa yankin cikin hatsari.
Ƙasashen Waje
Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza
![Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/5760.jpg)
Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza
Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.
KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar
Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.
Ƙasashen Waje
Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC
![Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/20261902_0-387-5446-3067.jpeg)
Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC
Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.
Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.
COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.
COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.
Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.
KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya
Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.
Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.
Ƙasashen Waje
An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran
![An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG-20240629-WA0085.jpg)
An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran
Daga Ibraheem El-Tafseer
Me magana da yawun Shelkwatar zaɓe ta Iran Dakta Muhsin Elsami, ya sanar da cewa, an kammala lissafi ƙuri’a Miliyan 25 na zaɓen shugaban ƙasar Iran wanda aka fara ranar juma’a.
‘Yan takara 6 ne suka tsallake matakin ƙarshe yayin da 2 suka fice saboda ra’ayin kai, ana zaɓe saura kwana 2.
Dakta Mas’ud Pezeshkian shi ne kan gaba da ƙuri’a Miliyan 10.415.991
Dakta Sa’ed Jalili ya samu ƙuri’u Miliyan 9.473298
Se kuma Dakta Qalibaf ya samu ƙuri’a Miliyan 3.383.340
Sai Ayatullah Musfata ya samu ƙuri’a 206.397.
Yanzu haka an fitar da Dakta Baqir Qalibaf da Ayatullah Musfata da suke da ƙarancin ƙuri’a, ya rage saura Dakta Jalili da Dakta Mas’ud Pezeshkian da ken gaba.
KU KUMA KARANTA: Iran ta tabbatar da mutuwar shugaban ƙasar, Ebrahim Ra’isi, a hatsarin jirgin sama
Jami’i Muhsin Elsami ya sanar da cewa za’a shiga matakin zaɓe na 2 ranar Juma’a mai zuwa inda za a kara tsakanin Dakta Jalili da Dakta Mas’ud.
Cikin su duk wanda ya samu kaso 50 ya zama shugaban ƙasar Iran, wanda zai maye gurbin Shahid Ebrahim Ra’isi wanda ya rasu sanadiyyar hatsarin jirgin Helikofta, a watan da ya gabata.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano