No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Uku daga cikin ƙasashen da sojoji suke jagoranta a yammacin Afirka sun ce za su fice daga ƙungiyar raya tattalin azriƙin yankin ta ECOWAS saboda takunkumin da aka ƙaƙaba musu.

Nijar da Mali da kuma Burkina Faso sun sanar da haka ne ta cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da aka karanta a gidan talabijin, suna cewa ECOWAS ta gaza taimaka musu wajen yaƙi da ta’addanci da kuma matsalar tsaro.

“Bayan shekaru 49, gwarazan al’umar ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar sun yi takaicin yadda ECOWAS ta sauƙa daga kan turbar da aka kafa ta, kamar yadda Kanar Amadou Abdramane, shugaban da ke jagorantar sojin da suka yi juyin mulki a Nijar ya karanta.

KU KUMA KARANTA: Firaiministan Nijar, Lamine Zeine, ya caccaki ECOWAS  kan yin zagon ƙasa

ECOWAS ta ƙaƙaba wa ƙasashen uku takunkumai tare da dakatar da su daga ƙungiyar, biyo bayan ƙwace iko da sojoji suka yi a jerin juyin mulkin da suka yi, abin da ya haifar da fargaba ta ɓangaren siyasa a Sahel.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...