No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

‘Yan tawayen Houthi sun kai wa tankar man Birtaniya da ke wucewa ta tekun Maliya hari da makami mai linzami.
Rahotonnin sun ce akwai ma’aikata 22 a cikin jirgin.

Jim kaɗan bayan harin ne, wani jirgin sojin ruwan Indiya da aka girke a yankin don yaƙar ‘yan tawayen ya fara mayar da martani.

Cikin wani saƙo da jami’an jirgin sojin ruwan suka wallafa a shafin sada zumunta, sun ce jirgin ya harba na’urar da ke kakkaɓo makami mai linzami don daƙile harin ‘yan tawayen kan tankar man Birtaniyar, bayan da ya samu ƙiran taimako.

KU KUMA KARANTA: Jirgi ya yi saukar gaggawa bayan fasinja ya gartsa wa ma’aikaciya cizo

A baya-bayan nan dai ana samun ƙaruwar hare-hare kan jiragen ruwa a tekun Maliya, bayan da ‘yan tawayen Houthi suka ce za su riƙa kai hari kan duk wani jirgin ruwan Isra’ila ko wanda ke kan hanyar zuwa Isra’ila, domin nuna adawarsu da hare-haren da Isra’ila ke kai wa Falasɗinawa Gaza.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...