No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya Antonio Guterres ya caccaki Kwamitin Tsaro na Majalisar bisa rashin bai wa Afirka kujerar mamba ta dindindin a cikinsa.

‘Ta yaya za a amince da matakin hana bai wa Afirka mamba ta dindindin a Kwamitin Tsaro?’ in ji Antonio Guterres a saƙon da ya wallafa a shafin X.

“Dole ne ƙungiyoyi su yi nazari kan halin da duniya take ciki a yau, ba abin da ya faru ba shekaru 80 da suka wuce. Taron da za a yi a watan Satumba zai bayar da wata dama ta duba batun sauye-sauyen shugabancin duniya da sake ƙulla alaƙa bisa gaskiya,” a cewarsa.

Guterres ya jaddada ƙiran da ya yi na kai kayan agaji da kuma tsagaita wuta a Gaza tare da sakin mutanen da aka yi garkuwa da su.

KU KUMA KARANTA: Australia ta goyi bayan ƙudurin MƊD na tsagaita wuta a Gaza

“Ba zan yi ƙasa a gwiwa ba wurin yin ƙira a tsagaita wuta nan-take da kai kayan agaji da kuma sakin dukkan mutanen da aka yi garkuwa da su ba tare da wasu sharuɗɗa ba,” in ji shi.

Da yake tsokaci kan halin da ake ciki a Gaza wadda ke ci gaba da fuskantar hare-haren Isra’ila, ya ce: “Al’ummar Gaza suna mutuwa sakamakon harin bama-baia da rashin abinci da wuta da kuma rashin hasken lantarki a asibitoci da rashin magunguna.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...