Tinubu ya gana da Ganduje, shugabannin APC na Jihar Kano

0
117

A ranar Alhamis ɗin nan ne shugaba Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri da tawagar da ta ƙunshi shugabannin jam’iyyar APC reshen jihar Kano a fadar Aso Rock Villa da ke Abuja.

Jagoran tawagar akwai Shugaban jam’iyyar APC kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Ganduje, wanda ya isa fadar Villa tare da tawagar mataimakinsa daya taba zama ɗan takarar jam’iyyar a zaɓen gwamnan jihar, Nasir Gawuna.

Taron na ranar Alhamis ya zo ne mako guda bayan da kotun ƙoli ta yanke hukuncin amincewa da babban abokin hamayyar Gawuna, Abba Yusuf na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, a matsayin zaɓaɓɓen gwamnan jihar.

KU KUMA KARANTA: Ƙungiyar ‘yan jarida a Yobe sun gana da shugaban majalisar jihar

A ranar 12 ga watan Janairu ne kotun koli ta mayar da Yusuf a matsayin gwamnan jihar Kano, inda ta soke hukuncin kotun daukaka kara da ta bayyana Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Ba a bayyana ajandar taron na ranar Alhamis ba kuma waɗanda suka halarci taron ba su yi magana da manema labarai na fadar gwamnati ba.

Leave a Reply