Gwamnan Kano ya bayyana kyautar N35,000 ga ma’aikata da ‘yan fansho a jihar

0
108

Gwamna Abba Kabir Yusuf ta sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da ƙungiyar kwadago ta Najeriya NLC da TUC domin bayar da kyautar N35,000 ga ma’aikata da ‘yan fansho a jihar.

Yarjejeniyar na nufin rage matsalolin tattalin arziki da ma’aikatan gwamnati ke fuskanta a jihar Kano bayan cire tallafin man fetur.

Comrade Mubarak Buba Yarima, shugaban ƙungiyar TUC reshen Kano ne ya tabbatar da hakan a ranar Talata, inda ya jaddada muhimmiyar rawar da ƙungiyoyin ƙwadago ke takawa wajen tattaunawa da gwamnati.

Yarjejeniyar ta samo asali ne biyo bayan roƙon haɗin gwiwa da NLC da TUC suka gabatar wa gwamnatin jihar Kano a watan Oktoban 2023, suna neman a shiga tsakani a cikin matsalolin tattalin arziki da ake fama da su.

A martanin da Gwamna Yusuf ya mayar, nan take ya kafa kwamiti na musamman domin tantance lamarin. Binciken kwamitin ya kai ga cimma matsaya kan cewa za a fara biyan N20,000 daga watan Disamba 2023 ga dukkan ma’aikatan gwamnati a matakin jihohi da ƙananan hukumomi.

KU KUMA KARANTA: Gwamnan Kano ya ƙaddamar da ayyukan gadar gadojin sama a jihar

Yarima ya ƙara da cewa za a ci gaba da bayar da tallafin kuɗi har sai an gudanar da cikakken nazari kan mafi ƙarancin albashi a cikin watanni shida masu zuwa.

Bugu da ƙari, masu karɓar fansho za su riƙa karɓar N15,000 duk wata na tsawon watanni uku, tare da biyan bashin alawus ɗin Disamba 2023 da suka rasa.

Yarima ya bayyana jin daɗinsa ga gwamnatin jihar Kano, musamman ma mai baiwa gwamna shawara kan harkokin ƙwadago, Kwamared Baffa Sani Gaya, da sauran mambobin kwamitin bisa gaggaruwar bincike da miƙa kai ga gwamnan.

Tun da farko dai ƙungiyoyin ƙwadago sun yi barazanar yajin aikin a faɗin ƙasar domin bayyana ƙalubalen da ma’aikata ke fuskanta bayan cire tallafin man fetur da shugaba Bola Tinubu ya yi.

Leave a Reply