No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mayakan Al-Qassam Brigades, wato ɓangaren soji na ƙungiyar Falasɗinawa ta Hamas, sun harba manyan rokoki daga Zirin Gaza zuwa birnin Tel Aviv na Isra’ila da garuruwan da ke kewayensa da sanyin safiyar Litinin, abin da ya sa jiniya ta yi ta kuka.

Gidan rediyon Rundunar Sojin Isra’ila ya ce haka kuma an harba rokoki a biranen Rishon Lezion, Lod, Ramla, Bnei Brak da Sderot baya ga wani matsugunin Yahudawa mai suna Modi’in Illit da ke tsakiyar Gabar Yammacin Kogin Jordan da aka mamaye.

A wani sako da suka wallafa a manhajar Telegram, mayaƙan Al-Qassam Brigades sun tabbatar da cewa sun harba bama-bamai a Tel Aviv da kewayensa.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun yi artabu da mayaƙan Hezbollah

“Al-Qassam Brigades na yin luguden wuta da makaman roka samfurin M90 a birnin Tel Aviv da kewayensa domin yin raddi ga kisan kiyashin da Yahudawa suke yi wa fararen-hula,” in ji sanarwar.

Kazalika sanarwar ta nuna bidiyoyin harin rokokin da ƙungiyar ta kai.

Babu bayani kan ko hare-haren sun yi sanadin mutuwa ko jikkatar wani ko wasu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...