Connect with us

Labarai

An kama mutane tara da zargin amfani da audugar mata da famfas wajen haɗa matashin-kai

Published

on

Hukumar tsaron farin kaya ta ƙasa, NSCDC, ta kama wasu mutane tara da suke haɗa wa da siyar da matashin kai da suke cika shi da famfas ɗin yara da audugar mata da akayi anfani da su a Sakwkwato.

Da ya ke gabatar da waɗanda ake zargin a hedikwatar rundunar a ranar Laraba, kwamandan jihar, Bello Alkali Argungun, ya ce kamasu ya biyo bayan rahoton sirri da su ka samu.

Ya ce, “Sun yi amfani da yara ƙanana da suke kawo musu shara. Sun cika kwandon matashin kai da shi wanda suke sayar wa kwastomominsu. Kayan matashin kan na ɗauke da tambari daban-daban na sanannun kamfanonin yin katifa.”

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sandan Kano sun kama mutum tara bisa zargin su da sayar da yara

A cewar Argungun, hakan na iya yin illa ga lafiyar masu amfani da matashin kan.

“Suna iya kamuwa da wasu cututtuka ba tare da sanin musabbabin hakan ba. Ina ƙira ga jama’armu da su rika zuwa kasuwa da suka dace domin sayen kayayyaki,” inji shi

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Kotu ta umarci Sadiya Farouq ta yi bayani kan yadda aka kashe biliyan N729 na tallafi

Published

on

Kotu ta umarci Sadiya Farouq ta yi bayani kan yadda aka kashe biliyan N729 na tallafi

Kotu ta umarci Sadiya Farouq ta yi bayani kan yadda aka kashe biliyan N729 na tallafi

Kotun Tarayyar da ke Legas ta umarci tsohuwar ministar ayyukan jin ƙai a gwamnatin Buhari wato Sadiya Umar-Farouq ta yi bayani kan yadda ta kashe naira biliyan 729 da gwamnatin ƙasar ta bai wa ‘yan Najeriya miliyan 24 a watanni shida na 2021.

Haka kuma kotun ta bayar da umarni ga tsohuwar ministar ta kawo jerin sunayen mutanen da aka biya kuɗin, da kuma jihohin da waɗanda aka biya kuɗin suka fito da kuma adadin da kowace jiha ta samu.

Ƙungiyar nan da ke yaƙi da cin hanci ta SERAP a Najeriya ce ta shigar da tsohuwar ministar ƙara inda ta buƙaci a yi bayani kan yadda aka raba kuɗin a zamanin Buhari.

Kotun ta bayyana cewa ƙungiyar da ta shigar da ƙarar ta buƙaci a ba ta bayanai dangane da kuɗin da aka raba wa ‘yan ƙasar a 2021.

Ƙungiyar ta SERAP ta yi jinjina ga hukuncin da alƙalin kotun Deinde Isaac Dipeolu ya yanke inda ya ce hakan “nasara ce ga gaskiya da riƙon amana wurin kashe kuɗaɗen jama’a.”

Tuni dai SERAP ɗin ta aika wasiƙa ga ofishin shugaban Nijeriya Bola Tinubu da kuma babban lauyan kasar domin su bi umarnin hukuncin da kotun ta yanke.

KU KUMA KARANTA: Shugabannin bankuna na amsa tambayoyi kan badaƙalar Beta Edu da Sadiya — EFCC

“Muna buƙatar ku umarci ma’aikatar jin kai da ta gaggauta tattara tare da fitar da bayanan kashe kudade na naira biliyan 729 (dala miliyan 467) kamar yadda kotu ta bayar da umarni,” in ji mataimakin daraktan ƙungiyar, Kolawole Oluwadare a ranar Asabar.

Continue Reading

'Yansanda

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Published

on

An ja hankalin 'yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ja hankalin ‘yan ƙasar game da shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi a faɗin ƙasar musamman a jami’o’i da manyan makarantu.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen Jihar Ribas Grace Iringe-Koko ce ta yi wannan jan hankali a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar da maraice a birnin Fatakwal.

Ta bayyana cewa wata babbar ƙungiyar asiri ta Najeriya tana shirin gudanar da gagarumin biki ranar Lahadi a faɗin Najeriya, musamman a jami’o’i don tunawa da mutumin da ya kafa ta.

“Rundunar ‘yan sandan Jihar Ribas ta samu bayanai game da bikin da ƙungiyar Neo-Black Movement (NBM) za ta yi a faɗin ƙasar ranar 7 ga watan Yulin 2024. Ƙungiyar, wadda ake yi wa laƙabi da Aiye ko Black Axe, tana shirin gudanar da bikin ne domin tunawa da wanda ya kafa ta.

KU KUMA KARANTA: Shugaban hukumar leƙen asirin sojin Isra’ila ya yi murabus saboda harin Hamas na 7 ga Oktoba      

Bikin, wanda aka sanya wa suna Ranar AIYE ko 7/7 za a gudanar da shi ne a dukkan jihohin da ke faɗin ƙasa, musamman a manyan makarantu,” in ji sanarwar.

An gargaɗi masu ta da hankalin jama’a a Bikin Dodanni na Egungun a Jihar Oyo

Rundunar ‘yan sandan ta ce tana sane da munanan ayyukan ƙungiyar asirin na kisan mutane a manyan makarantu da faɗace-faɗace a tsakanin ƙungiyoyin asiri da tayar da zaune-tsaye da sauran manyan laifuka.

Ta ce yanzu haka ta baza ƙarin jami’an ‘yan sanda zuwa wasu wurare domin daƙile ayyukan ƙungiyoyin asiri, sannan ta yi ƙira ga iyaye su gargaɗi ‘ya’yansu su guji shiga ayyukan ƙungiyoyin asiri.

“Ana bai wa manyan makarantu shawarar ƙara matakan tsaro da kuma sanya idanu sosai domin tabbatar da tsaron dukkan ɗalibai.

Kazalika ana ƙira ga dukkan makarantu su lura da duk wani taro na ɗalibai da bai kwanta musu a rai ba,” a cewar sanarwar.

Continue Reading

Labarai

An sake zaɓen Bola Tinubu a matsayin shugaban ECOWAS

Published

on

An sake zaɓen Bola Tinubu a matsayin shugaban ECOWAS

An sake zaɓen Bola Tinubu a matsayin shugaban ECOWAS

Daga Idris Umar, Zariya

An tsawaita wa’adin Shugaban ƙungiyar ne a taron shugabannin ƙungiyar ECOWAS karo na 65 da aka yi a ranar Lahadi a Abuja, biyo bayan matakin da Shugabannin suka ɗauka na tabbatar da dorewar zaman lafiya da samar da ci gaba.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai ba Shugaban ƙasar Najeriya kuma Shugaban ECOWAS shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai Cif Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu, kuma aka rabawa manema labarai.

Da farko dai an zaɓi Shugaba Tinubu a matsayin Shugaban Ƙungiyar a Guinea Bissau a ranar 9 ga Yulin 2023.

A jawabinsa na karɓar Shugabancin ya ce, zai mayar da hankali wajen ƙarfafa kimar dimokaradiyya da kuma tabbatar da muradun ƙungiyar da za ta cika shekaru 50 a shekarar 2025.

Shugaban ƙungiyar ECOWAS ya ayyana Shugaban ƙasar Senegal Bassirou Diomaye Faye, da shugaban kasar Togo Faure Essozimna Gnassingbé a matsayin jakadu na musamman da za su maido ƙasashen Burkina Faso, da Mali, da Jamhuriyar Nijar cikin ƙungiyar bayan ficewarsu.

“Zan ci gaba da ɗaukar matakan cigaba, gami da gina tsarin dimokuradiyya da tsarin da muka gada Na gode sosai ”Shugaban ya ce.

A baya dai Shugaba Tinubu ya yi kira ga shugabannin kasashen kungiyar ECOWAS da su ba da himma wajen ganin an kafa rundunar da za ta samar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin yankin.

KU KUMA KARANTA: Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugaban ya jaddada amfanin rundunar da za ta yi aiki tare da fuskantar barazanar tsaro a yankin.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like