No menu items!

Sample Page Title

Date:

’Yan bindiga sun sace manoma 11 a yankunan Achimbi da Gumanyi da ke Kwaku a yankin Kuje a Abuja.

Wani mazaunin Achimbi, Yunusa Aliyu, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Juma’ar da misalin karfe 11:00 na safe lokacin da manoman suke girbin doya a gonakinsu.

Ya ce ’yan bindigar ɗauke da muggan makamai ba zato ba tsammani suka kewaye su, nan take suka yi awon gaba da su.

Aliyu, ya ce ’yan bindigar sun fara sace wani manomi a wata gona da ke Gumanyi kafin su wuce Achimbi su yi awon gaba da wasu 10 a can.

Ya ce ya zuwa yanzu maharan ba su tuntuɓi iyalan waɗanda suka sace ba, domin neman kuɗin fansa.

KU KUMA KARANTA: Yankunan Bwari, Kuje da Abaji suka fi haɗarin rayuwa a Abuja – FCTA

Ya ƙara da cewa shugaban maharan ya ce ba zai yi magana game da kuɗin fansa ba har sai ya gana da shugaban ƙauyen Achimbi.

“Kuma yanzu mun ruɗe saboda shugabansu ya ce ba zai yi magana game da kuɗin fansa ba har sai ya gana da shugaban ƙauyenmu.

“Kuma shugaban ƙauyen nan ya yi tafiya ba ya nan, duk da cewa ana sa ran zai dawo yau Lahadi ko Litinin,” in ji shi.

Lokacin da aka tuntuɓi, kakakin rundunar ’yan sandan birnin tarayya, SP Adeh Josephine, ta ce ba ta da masaniyar faruwar lamarin.

Amma ta yi alƙawarin yin ƙarin haske da zarar ta samu bayani.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...