No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’an lafiya na Falasɗinu sun ce wasu hare-hare ta sama da Isra’ila ta kai a jajiberin Kirsimeti sun yi sanadin mutuwar mutum aƙalla 78.

Isra’ila ta ƙaddamar da hare-haren ne da tsakar daren Litinin inda ta wayi garin yau tana luguden wuta musamman a yankin Al Bureij da ke tsakiyar Gaza, kamar yadda ganau da kafafen watsa labarai na Falasɗinu suka tabbatar.

An kashe aƙalla mutum 70 a hari ta sama da jiragen yakin Isra’ila suka kai yankin Maghazi da ke tsakiyar Gaza, a cewar mai magana da yawun ma’aikatar lafiyar Falasɗinu Ashraf Al Qidra, yana mai cewa galibinsu mata ne da ƙananan yara.

KU KUMA KARANTA: An kashe sojojin Isra’ila takwas a Gaza, an yi wa shida mummunan rauni

Rundunar sojin Isra’ila ta ce tana nazari kan abin da ya faru a Maghazi kuma tana so ta rage yawan fararen-hular da ke cutuwa. Ƙungiyar Hamas ta musanta zargin da Isra’ila ke yi mata cewa tana buya a wuraren da ke da dandazon jama’a inda take yin amfani da mutanen a matsayin garkuwa.

Ƙungiyar agaji ta Palestinian Red Crescent ta wallafa bidiyoyin mutanen da suka jiakkata a yayin da ake tafiya da su asibiti. Ta ce jiragen yaƙin Isra’ila sun yi ta luguden wuta a manyan hanyoyin da ke tsakiyar Gaza, inda suka hana motocin ɗaukar marasa lafiya wucewa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...