No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’an hukumar Hisbah na jihar Kebbi sun sami ‘yan mata yara ƙanana guda biyu suna gararamba a garin Birnin kebbi.

Wannan na ƙunshe a wata sanarwa da hukumar ta wallafa ranar Asabar 23 ga watan Disamba 2023.

Sanarwar na ɗauke da cewa:

“ANSAMU ƘANANAN YARA MATA SU BIYU SUNA GARARANBA A BIRNIN KEBBI

Hukumar Hisbah ta samu Yara ‘yan mata guda biyu, ɗaya mai suna Aisha lawali jah ‘yar ƙauyen magazu unguwar sabon layi dake tsafe local govt zamfara state.

KU KUMA KARANTA: Hisbah ta kama ɗan acaɓa da ya yi wa yar shekara 12 fyaɗe

Sai ɗayar kuma mai suna Nasmatu Abdullahi gwangwala, ‘yar ƙauyen kunduttu dake maiyama local govt jihar kebbi 

Duk kansu sun zo yawo ragaita ne garin Birnin Kebbi. Hukumar Hisbah ta jihar kebbi ta zanta da hukumar Hisbah ta zamfara don gano iyayen Aisha magazu don sadata dasu.

Haka ma hisbah ta zanta da kakan Nasmatu dake ƙauyen unguwar kurya ta maiyama shikuma yana cikin yanayin rashin lafiya da bazai iya zowa ba don tace babanta ya rasu mamarta na aure barkeji ta jihar sokoto

Allah ya shiryadda zuriar mu yayi muna tsari ameen”.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...