No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani ɗan sanda mai muƙamin Sufeto ya kashe abokin aikinsa sannan ya harbe kansa har lahira.

Wannan ƙarar kwana ya faru ne ranar Lahadi a ƙauyen Nyogor-Lueku, ƙaramar Hukumar, Jihar Ribas.

Aminiya ta samu bayani cewa ’yan sandan biyu suna aiki ne a caji ofis da ke Taabaa, lokacin da suka tafi aiki Nyogor-Lueku su kamo wani mutum bisa wasu tuhume-tuhume da mahaifiyarsa ta kawo ƙara ofishin.

Kazalika ana zargin sa da bijire wa umarnin gayyatar da aka yi masa, al’amarin da ya kawo ce-ce-ku-ce tsakaninsa da jami’an.

Majiyar labarinmu ta ce “Ana tsaka da wannan cacar baka sai cikin kuskure Sufeto Nelson Abuante ya yi harbi ya samu abokin aikinsa Gbaramana, ya ji mummunan rauni

“A sakamakon haka sai Abuante da mahaifiyar mutum da aka je ƙara suka gaggauta ɗaukar sa zuwa asibiti a cikin mota, amma sai mai ya kare a hanya, ta wannan dalili me Sufeto Monday ya ce ga garin ku nan.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda a Gwambe, sun kama matashin da ya kashe wata mata mai shekaru 58

“Har-wa-yau ganin abokin aikinsa ya mutu, shi ma Sufeto Abuante ba tare da jinkiri ba ya sanya bindigarsa ya harbe kansa.”

Wakilin mu ya tuntuɓi kakakin rundunar Grace Iringe-Koko, kuma ta tabbatar da hakan ya afku, ta kara da cewa “An kafa kwamitin bincike a kan lamarin.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...