No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Sudan ta bai wa ma’aikatan diflomasiyyar Chadi wa’adin awa 72 su fita daga ƙasar a wani mataki na taɓarɓarewar hulɗa tsakanin ƙasashen biyu.

Kafar watsa labaran ƙasar ce ta bayyana haka ranar Lahadi.

Ta ambato hukumomin Sudan suna cewa jami’an diflomasiyyar na Chadi sun rasa martaba ta ci gaba da zama a Khartoum, don haka dole su tattara kayansu su fita daga ƙasar, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito.

Sai dai ba a bayyana sunaye da muƙaman jami’an diflomasiyyar da aka kora daga Sudan ba.

A nata ɓangaren, Chadi ta kori ma’aikatan diflomasiyyar Sudan da suka haɗa da babban jami’in diflomasiyya a ofishin jakadancin Sudan da ke Chadi, da babban jami’in tsaron ofishin da kuma ma’aikata biyu, kamar yadda gwamnatin Chadi ta bayyana ranar Asabar.

KU KUMA KARANTA : Ƙasar Chadi ta kori ma’aikatan diflomasiyyar Sudan

An ɗauki matakin ne bayan wani babban jami’in sojin Sudan Janar Yassir al-Attaya ya yi “kalamai masu nauyi marasa dalili,” sannan shi ma ministan harkokin wajen Sudan ya maimaita su a wani gidan talbijin, in ji sanarwar da kakakin gwamnatin Chadi ya fitar.

“Waɗannan kalamai da jami’in gwamnatin Sudan suka yi a kan Chadi da gwamnatin ƙasarmu ba abu ne da za mu amince da shi ba , kuma suna tunzura jama’a sannan cike suke da wata kullalliya,” a cewar sanarwar.

Yaki ya barke a Sudan tun watan Afrilu tsakanin dakarun sojin kasar da na rundunar Rapid Support Forces (RSF) lamarin da ya yi sanadin kisan dubban mutane, sannan miliyoyi suka tsere daga gidajensu, ciki har da dubbai da suka tsallaka cikin Chadi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...