Hezbollah ta ce ta halaka sojojin Isra’ila da dama a wani hari kan sansaninsu

0
203

Ƙungiyar Hezbollah ta Lebanon a ranar Asabar ta ce ta kai hari kan sansanin sojin Isra’ila na Birket Rishe da ke kan iyakar ƙasar Lebanon da Isra’ila inda ta ce ta halaka sojojin da dama da raunata wasu.

Ƙungiyar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar inda ta ce ta yi amfani da makamai mai linzami wurin kai harin.

Rikici tsakanin Hezbollah da kuma sojojin Isra’ila ya ƙara ƙazanta tun bayan da yaki ya rincaɓe tsakanin sojojin Isra’ila da dakarun Hamas a ranar 7 ga watan Oktoba.

Leave a Reply