Wani matashi ya kashe mahaifiyarsa

0
135

Wani matashi mai suna da Sadiq Idrissu, ya kashe mahaifiyarsa a Jihar Adamawa, kuma ya bayyana cewa bai yi nadamar kisan gillar da ya yi mata ba.

Alfijir labarai ta rawaito matashin mai shekaru 30, ya kashe mahaifiyarsa ne ranar 05 ga watan Disemba 2023, a garin Boga cikin ƙaramar hukumar Gombi a jihar, maimakon nadama kan kisan gillar da yai mata, amma cewa “ban yi nadamar kisan da na yi wa mahaifiyata ba” in ji matashin.

KU KUMA KARANTA: Ɗan kasuwa ya nemi kashe matarsa don ya ƙara jari a shagonsa

Ya ci gaba da cewa “na kashe ta ne, saboda ta bayyana min ita mayya ce, da ma jama’a na zarginta da maita, kuma gaskiya ne, domin tana aikata wasu abubuwan mamaki, musamman da daddare.

“Mamana tana bayyana min a cikin mafarki a matsayin mayya, tana kuma jefa min tsoron da ke hana ni yin bacci da daddare” in ji matashin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here