No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC) a Jihar Zamfara ta tabbatar da mutuwar mutum shida a Gusau, sakamakon wani hatsarin mota.

Kwamandan hukumar a jihar, Iro Danladi, ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) a Gusau a ranar Talata.

Ya bayyana cewa ya kamata a wayar da kan mutane game da gyaran tituna da ake yi a jihar.

Waɗanda abin ya shafa galibin mata ne da yara ƙanana da ke tsallaka titi.

KU KUMA KARANTA: Mutum 16 sun mutu, 27 sun jikkata a hatsarin tirela a Kaduna

Danladi ya gargaɗi direbobi da su yi taka-tsan-tsan tare da rage gudu don guje wa yanayin da ba a shirya masa ba.

A cewarsa, duk da cewa ma’aikatan hukumar suna kan hanyoyin don saukaka zirga-zirga, amma akwai bukatar kamfanonin gine-ginen da ke gudanar da ayyukan tituna a jihar su samar da isassun alamun hanyoyin don jan hankalin masu ababen hawa da jama’a.

Ya yi ƙira ga gwamnati da ta faɗakar da jama’a kan yadda za a yi amfani da hanyoyi a wannan lokaci na ayyukan gyaran tituna, la’akari da sauye-sauyen tsarin zirga-zirga.

Danladi ya ce ya kamata gwamnati ta ɗauki nauyin wayar da kan jama’a a kafafen yaɗa labarai game da hanyoyin da ake gyara don kauce wa rasa rayuka da dukiyoyi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...