No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hatsarin tirela ya yi ajalin mutane 16 yayin da wasu 27 suka samu raunuka a jihar Kaduna.

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) a jihar, Kabir Nadabo ya ce hatsarin ya auku ne ranar Lahadi.

Nadabo ya ce wata tirela kirar DAF dauke da mutane 65 ce ta kwace ta fada a cikin wani rami da asuba.

Ya bayyana cewa hatsarin ya faru ne a kusa da ƙauyen Audu Jangwam a kan Babbar Hanyar Kaduna-Abuja.

Yana yi zargin hatsarin ya auku ne a sakamakon gudun wuce ƙa’ida da kuma gajiyar direba.

KU KUMA KARANTA: Hatsarin tirela ya yi ajalin mutum 11 a Kebbi

Ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) cewa an kai waɗanda suka jikkata asibiti

Jami’an hukumar na aikin ceto domin kawar da motar, wadda ta ɓarinta ya tare hanyar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...