No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sanatocin Najeriya gaba ɗayansu sun sadaukar da albashinsu na watan Disamba ga mutanen da harin bom da jirgin soji ya samu a wurin taron Mauludi a Jihar Kaduna.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin ya sanar cewa sanatocin su 109 sun amince a ba da albashin nasu a matsayin gudunmuwar ga mutanen Tudun Biri.

Sanata Barau wanda ya yi bayani a yayin ziyararsu fadar gwamnatin Kaduna domin jajanta wa Gwamna Uba Sani  kan tsautsayi, ya bayyana cewa albasjin ya kama naira miliyan 109.

Ya ce hakika sun yi baƙin ciki bisa tsautsayin da ya auka wa al’ummar garin na Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi, kuma majalisar ta sha alwashin yin bincike domin gano musabbabin abin da ya faru.

KU KUMA KARANTA: Za mu jajirce har sai an yi wa mutanen Tudun-Biri adalci – Sarkin Musulmi

Gwamna Uba Sani a jawabinsa ya miƙa godiyarsa ga dukkan ’yan majalisar da suka jajanta masa, inda ya buƙaci su tabbatar da Hakimin Yan Tudun Biri ya fito kunya ta hanyar yi musu adalci.

Ya kuma nuna rashin jin daɗinsa bisa yadda wasu ke neman sanya rigar addini ko ƙabilanci a kan abin da ya faru, inda ya ce abin ba haka yake ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...