No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan Katsina, Dikko Raddah, ya jagoranci fatattakar ’yan bidiga a ƙauyen Zakka a ƙaramar hukumar Safana ta jihar.

Gwamnan ya jagoranci jami’an tsaro haɗin gwiwa wajen ceto wani matashi da ’yan bindiga suka yi garkuwa da shi.

Dikko Radda ya jagoranci kai ɗaukin ne a lokacin da ya je ƙaramar hukumar ƙaddamar da shirin tallafi na mataimakin shugaban majalisar jihar,  Abduljalal Runka.

Sakataren yaɗa labaran gwamna, Kaula Mohammed, ya ce kafin ƙaddamar da tallafin ne jami’an tsaro suka samu ƙiran gagawa cewa ’yan ta’adda sun kai hari ƙauyen Zakka.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito Kaula na cewa, nan take gwamnan ya dakatar da shirin, shige gaba aka fatattaki ’yan bindigar, aka ceto matashin.

Daga nan gwamnan ya ba da umarnin kai mutumin asibiti domin kula da shi, saboda harbin sa da aka yi a kafa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...