Ya kashe kawunsa kan zargin maita a Adamawa

0
162

Wani mutum ya kashe kawunsa kan zargin maita a yankin Dumna Zarbu da ke ƙaramar hukumar Guyuk ta jihar Adamawa.

Wanda ake zargin mai shekaru 42 dai ya musanta aikata laifin da aka gurfanar da shi a kai.

Shaida sun ce  mamacin ya rasu ne bayan ɗan nasa ya buge shi da sanda saboda an zarge shi ne da kisan wasu mutane ta hanyar maita, zargin da ya musanta.

Bayan sauraron ƙarar ne alkali Alheri Ishaku ta babbar kotun majistare ta ɗaya da ke Yola ta ba da umarnin tsare wanda ake zargi da kisan a gidan yari.

Daga nan ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 4 ga watan Janairu, 2024.

Leave a Reply