No menu items!

Sample Page Title

Date:

Yukiren ta ce ta kakkaɓo jirage marasa matuki guda 71 da Rasha ta kai mata hari da su a cikin dare, harin da ta bayyana a matsayin mafi girma tun bayan da Rasha ta ƙaddamar da mamaya a kanta.

Rundunar sojin Yukiren ɗin ta ce akasarin jiragen ƙirar Iran ne, kuma ta kakkaɓo su ne a baban birnin ƙasar, Kyiv, lamarin da ya haddasa ɗaukewar wutar lantarki, a yayin da yanayin sanyi a ƙasar ya tsananta.

Tun da farko ta ce ta kakkaɓo jirage 71 daga cikin 75 da aka kai mata hari da su, daga baya kuma ta ce ta harbo 74. A wani jawabi da ya  yi ta talabijin, Kakakin sojin saman ya ce 66 daga cikin jiragen da suka kaddamar da harin an kakkaɓo su ne a Kyiv da garuruwan da ke kewayen sa.

KU KUMA KARANTA: Rasha ta harbo jiragen Yukiren marasa matuƙa 31 a yankunan kan iyaka

Harin jirage marasa matukan na zuwa ne a daidai lokacin da Yukiren ke bikin tunawa da ranar Holodomor,  lokacin da miliyoyin mutane suka shiga yanayi na tsananin yunwa a shekarar 1930 ƙarƙashin shugaba Josef Stalin na Tsohuwar Tarayyar Soviet.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...