No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Haruna Idi Hassan

Jam’iyyar APC a jihar Kano ta buƙaci ɗaukacin mambobinta da ƴan kasuwar da suka yi asarar dukiyarsu sakamaƙon rushe musu shaguna da gidaje da gwamnatin jihar ta yi da su fara azumi a yau.

Shugaban jam’iyyar, Abdullahi Abbas, a cikin wani saƙon murya ya buƙaci da su yi addu’a tuƙuru domin nuna godiya ga nasarar da jam’iyyarsu ta samu nasara a ƙotun dauƙaka ƙara a ranar Juma’a.

Saƙon nasa na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf na Jam’iyyar NNPP, ya yanke hukuncin ƙalubalantar hukuncin kotun dauƙaka ƙara a gaban kotun ƙoli.

A wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun babban sakataren yaɗa labaransa, Sanusi Bature Dawakin Tofa, gwamnan ya ce ya umarci lauyoyinsa da su ɗaukaka ƙara kan hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara ta yanke.

KU KUMA KARANTA: Saƙon Dr. Nasiru Gawuna ga al’ummar Kano bayan hukuncin kotun ɗaukaka ƙara

Ya ƙara da cewa yana da ƙwarin gwiwar cewa “Kotun ƙoli za ta sauke hukuncin da yardar Allah.”

Tun da fari kotun sauraron ƙararrakin zaɓe ta fara soke Abba, hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar daga bisani.

Hukunci biyu sun haifar da zazzafar muhawara musamman a tsakanin masu sharhi kan al’amuran siyasa a jihar.

Kazalika, hukuncin ya haifar da cece-ƙuce da fargaba a tsakanin mazauna jihar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...