No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙungiyar Hezbollah ta ƙasar Lebanon ta ce ta kakkaɓo jirgin Isra’ila maras matuƙi da makami mai linzami a yankin Galilee Panhandle.

Ƙungiyar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar a ranar Asabar da safe inda ta ce ta harba makamin nata da misalin karfe 1:45 agogon ƙasar, (23:45 agogon GMT).

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta ƙi amincewa da ƙudirin MƊD na tsagaita wuta

Ta bayyana cewa ta hango lokacin da tarwatsatsun sassan jirgin ke faɗawa a yankin Galilee Panhandle.

Har yanzu Isra’ila ba ta fitar da sanarwa domin gasgatawa ko kuma karyata iƙirarin na Hezbollah ba.

Sama da Falasɗinawa 12,000 Isra’ila ta kashe zuwa yanzu, inda sama da 8,300 yara ne da mata, haka kuma ta raunata sama da 30,000.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...