No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja babban birnin Nijeriya ta tabbatar da Nasiru Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin halastaccen gwamnan Kano a zaɓen watan Fabrairun 2023.

Kotun ta kuma buƙaci Gwamna Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP ya mika mulki ga Gawuna.

Ta bayyana haka ne a hukuncin da ta yanke ranar Juma’a.

Kotun ta tabbatar da hukuncin da kotun sauraren ƙararrakin zaɓe ta jihar Kano ƙarkashin jagorancin Mai Shari’a Oluyemi Akintan Osadebay ta yanke wanda ya sauke Abba Kabir Yusuf daga mukamin gwamnan jihar ranar 20 ga watan Satumba.

Kotun ta cire ƙuri’a 165,663 daga ƙuri’un da Abba Gida-Gida ya samu inda ta ce ba su da inganci, tana mai cewa ba a manna wa ƙuri’un 165,663 hatimi ba don haka ba sahihai ba ne.

KU KUMA KARANTA: An baza ƙarin sojoji da ‘yan sanda a Kano gabanin hukuncin kotu kan shari’ar Abba da Gawuna

Sai dai jim kaɗan bayan hakan, Abba Kabir Yusuf na Jam’iyyar NNPP ya shigar da ƙara inda yake kalubalantar hukuncin kotun.

Tun da farko a zaɓen da aka yi a watan Maris ɗin 2023 Abba Kabir Yusuf na Jam’iyyar NNPP ya samu kuri’u 1,019,602, sai kuma Nasiru Yusuf Gawuna na APC ya samu 890,705.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...