No menu items!

Sample Page Title

Date:

Aƙalla mutum 32 da suka haɗa da yara 20 da manya 12 ne suka rasa rayukansu a wani hatsarin kwale-kwale a garin Ibbi da ke ƙaramar hukumar Ibbi a jihar Taraba.

Kwale-kwalen na ɗauke da masunta sama da 50 daga garin Ibbi zuwa Gabashin jihar a ranar asabar don yin su a yayin da ya kife a kusa da gaɓar kogin Benuwai.

Wani mazaunin garin Ibbi, Malam Ibrahim Ibbi, ya ce yara 20 da manya 12 ne suka mutu a hatsarin.

Gwamnan jihar, Agbu Kefas, ya bayyana lamarin a matsayin abun taƙaici, kwanaki kaɗan bayan faruwar wani hatsarin jirgin ruwan a Karim Lamido.

Ya jajanta wa al’ummar Ibbi tare da addu’ar Allah Ya jikan waɗanda suka rasu.

KU KUMA KARANTA: Manoma 4 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Nasarawa

Gwamna Kefas, ya ce gwamnati ta tashi tsaye wajen gudanar da bincike domin gano musabbabin yawan hatsarin kwale-kwale a jihar.

Gwamnan ya ce nan ba da jimawa da kansa zai zagaya yankunan da abin ya shafa da nufin ganawa da masu ruwa da tsaki a harkar sufurin ruwa.

Kazalika ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki don ƙare rayukan al’ummar jihar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...