No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jam’aa sun yi wa wani lakcara kuma fasto duka tare da neman yi masa tsirara kan zargin satar mazakuta a yankin Wurukum da ke garin Makurdi a Jihar Binuwai.

Dokta Emmanuel Aime, wanda malami ne a Kwalejin Kimiyya da Kere-kere ta Akawe Torkula da ke jihar, ya je yin wa’azi ne a safiyar laraba a kusa wa wani banki inda wani ya yi kururuwa cewa an sace masa mazakuta.

Mutanen da suka ritsa shi, sun bayyana cewa fitowar Dokta Emmanuel daga cikin banki ke da wuya wani matashi ya yi ihu da zargin shi da sace masa mazakuta.

Nan take mutane suka far masa da duka suka yi masa jina-jina suka yayyaga kayansa, saura ɗan kamfai kafin sojoji da wasu jami’an tsaro suka yi suka kwace shi.

KU KUMA KARANTA: An yi wa ‘yan sanda biyar duka a Abuja, a ƙoƙarin ceton wanda ake zargi da satar mazakuta

Wani shaida a wurin ya ce daga baya an binciki matashin da ya yi zargin an sace masa mazakuta, amma aka same shi lafiya, shi ne aka garzaya da shi ofishin ’yan sanda.

Mai magana da yawun ’yan sandan jihar, SP. Catherine Anene, ta tabbatar da faruwar lamarin, wanda ta bayyana takaicinta a kansa

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...