Isra’ila ta sake kai harin bama-bamai a asibitocin Al Shifa da Al Nasr na Gaza

0
139

Jiragen yaƙin Isra’ila sun yi lugudan wuta a asibitin Al Shifa da asibitin yara na Al Nasr da ke Gaza.

A cewar kamfanin dillancin labarai na Falasɗinawa WAFA, Isra’ila ta harba rokoki a asibitin Al Shifa, inda dubban majinyata da ‘yan gudun hijira suke samun mafaka.

Harin da jiragen suka kai kusa da asibitin yara na Al Nasr da ke yammacin Gaza ya yi sanadin mutuwar Falasɗinawa uku da jikkata da dama.

Leave a Reply