No menu items!

Sample Page Title

Date:

Aƙalla mutum 12 ne ajali ya katsewa hanzari ciki har da yara biyu sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da su a ƙaramar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.

Lamarin, kamar yadda wani ganau ya shaida wa wakilinmu, ya ce ya faru ne da misalin ƙarfe 1:20 na rana a kan babbar hanyar Funtuwa zuwa Tsafe.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, hatsarin ya rutsa da mutum 24 — 22 a cikin wata motar haya da wasu mutum biyu a wata A-Kori-Kura ƙirar Toyota.

Hatsarin wanda ya auku a sakamakon tsautsayi, bayanai sun ce an yi taho-mu-gama ne tsakanin motocin yayin da gudanarwar motar hayar ta ƙwace daga hannun direbanta.

Yanzu haka dai an kwantar da waɗanda suka jikkata a Babban Asibitin Tsafe, inda suke karɓar magani.

KU KUMA KARANTA: Mutane bakwai sun mutu, 40 sun jikkata a wani hatsarin mota a Yobe

Wani jami’in Hukumar Kiyaye Haɗurra ta ƙasa (FRSC) da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya alaƙanta aukuwar hatsarin da tuƙin ganganci.

“Ina cikin jami’an FRSC da suka kai ɗauki wurin da hatsarin ya faru wanda ya rusta da mutum 24 a duk motocin biyu.

“Waɗanda suka mutu sun haɗa wasu mutum 10 da ƙananan yara biyu, yayin da kuma da dama suka jikkata,” a cewarsa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...